1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Taron kasuwaci tsakanin Indiya da Afirka

Ahmed SalisuOctober 24, 2015

Wakilan kasashe kimanin 50 sun fara hallara a Indiya domin halartar wani taro tsakanin kasar din da kasashen Afirka wanda zai maida hankali kan sha'anin cinikayya.

https://p.dw.com/p/1GtcQ
Indien Ministerpräsident Narendra Modi
Hoto: UNI

Taron wanda shi ne irinsa na uku kuma mafi girma da Indiya din za ta jagoranta zai maida hankali ne kan yaukaka huldar cinikayya da kuma diflomasiyya tsakanin kasar da kasashen Afirka.

Masu aiko da rahotanni suka ce baya ga batun cinikayya, taron har wa yau zai tabo abubuwan da suka danganci makamashi da tsaro da kuma magance dumamar yanayi.

Wannan dai na zuwa ne daidai lokacin da China wadda ke kan gaba ta fuskar cinikayyya da Afirka ta bayyana cewar ta na samun koma baya na cigaban tattalin arzikinta, lamarin da ya sanya ake ganin za ta ja baya kan hulda da kasashen Afirka a fage na kasuwanci.