1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Taron sulhunta rikicin siyasar Togo

May 28, 2006
https://p.dw.com/p/BuwQ

Wakilin mussamman na Majalisar Sinkin Dunia mai kulla da yankin yammacin Afrika, na ci gaba da tantanawa, da ɓangarori daban daban na ƙasar Togo, da zumar samar da masalaha, a rikicin siyasar wannan ƙasa.

Ahmedou Ould Abdallah, ya sauka juma´ar da ta wuce a birnin Lome.

Tun ranar 21 ga watan da ga ya gabata, yan siyasar Togo, su ka koma tebrin shawara, domin cimma daidaito a kan wani daftari, da zai samu amincewar ɓangarori masu gaba da juna.

A yanzu haka, ƙiddidigar hukumar Majalisar Ɗinkin Dunia mai kulla da yan gudun hijira, ta nunar da cewa, akwai a ƙalla yan gudun hijira na ƙasar Togo, kimanin dubu 20, da ke zaune a Benin, sakamakon rikicin siyasa, da ya wakana ƙasar, a watan Aprul na shekara bara.