1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Taron Tarayyar Turai bayan ficewar Birtaniya

Suleiman BabayoJune 25, 2016

Kasashen da suka jagoranci kafa Tarayyar Turai suna taro a Jamus bayan kuri'ar raba gardama da ta janyo ficewar Birtaniya daga kungiyar.

https://p.dw.com/p/1JDUq
Deutschland Berlin Brexit Treffen Außenminister EU Gründungsstaaten
Hoto: picture-alliance/AP Photo/M. Schreiber

Kasashen da suka kafa Tarayyar Turai suna taro a birnin Berlin na nan Jamus a wannan Asabar, domin duba makomar kungiyar bayan kuri'ar da Birtaniya ta kada na ficewa daga cikin kungiyar.

Ministan harkokin wajen Jamus Frank-Walter Steinmeier zai karbi bakoncin na Faransa, da Holland, da Italiya, da Belgiyam, da kuma Luxemburg da suka jagoranci kafa kungiyar. Tuni Tarayyar Turai ta nemi fara tattaunawa kan ficewar Birtaniya cikin hanzari ba tare da jira sai Firaministan Birtaniya David Cameron ya ajiye madafun iko ba cikin watan Oktoba mai zuwa.

A wani labarin kuma Shugaba Barack Obama na Amirka ya tabbatar da cewa kasar za ta ci gaba da dangantaka ta musamman da Birtaniya, duk da kuri'ar raba gardama da ta kawo karshen Birtaniya cikin kungiyar kasashen Turai.