1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Taron tunawa da harin Charlie Hebdo

Gazali Abdou TasawaJanuary 5, 2016

Francois Hollande ya jagorancin taron kaddamar da wasu alluna guda uku masu dauke da sunayen mutanen da suka mutu a harin da aka kai cibiyar jaridar Charlie Hebdo.

https://p.dw.com/p/1HYDo
Frankreich Hollande enthüllt Gedenktafel für den ermordeten Polizisten Ahmed Merabet in Paris
Hoto: Reuters/B. Tessier

Shugaban Faransa Francois Hollande ya kaddamar da taron tunawa da mutanen da suka rasu a cikin harin ta'addancin da aka kai a cibiyar jaridar Charlie Hebdo da ya yi sanadiyyar mutuwar mutane 17 a ranar bakwai ga watan Janerun shekara ta 2015.

Hollande ya jagorancin taron inda ya kuma kaddamar da wasu alluna guda uku masu dauke da jerin sunayen mutanen da suka mutu a cikin harin. Allunan da aka kafa a gurin da aka kashe 'yan jaridar da kuma a titin da daya daga cikin maharan ya hallaka wani dan sanda mai suna Ahmed Merabet da kuma a kusa da babban shagon Casher na gabashin birnin Paris inda wani shima mai tsananin kishin addinin mai suna Amedy Coulibaly ya hallaka wasu Yahudawa uku da suka je cefane a kantin na Cacher a ranar tara ga watan Janerun shekarar ta 2015.

A ranar Lahadi mai zuwa ce Faransar za ta gudanar da gagarumin taron nuna alhini ga mutanen 17 da suka rasu a cikin harin na Charlie Hebdo dama wasu mutanen 130 da suka mutu a cikin harin birnin Paris na ranar 13 ga watan Nuwambar shekarar da ta gabata.