1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Tashe tashen hankulla a ƙasar Irak

March 2, 2006
https://p.dw.com/p/Bv6H

A Irak tashe tashen hankulla na ci gaba da ƙara bazuwa a faɗin ƙasar bakin ɗaya, tun bayan da wasu mutane su ka kai hari, ga ɗaya, daga wuraren ibadar yan ɗarikar Shi´a a ƙarshen watan da ya gabata.

Ya zuwa yanzu, ɗaruruwan mutane, sun rasa rayuka a cikin hare haren ramuwar gayya, tsakanin yan Sunni da yan shi`a.

A sahiyar ƙarin sojoji da jami´an yan sanda fiye da 10 sun kwanta dama a cikin wani harin ta´adanci a arewancin Bagadaza.

A ci gaba kuma da shari´ar tsofan shugaba ƙasa, Saddam Hussain, a karro na farko, ya bayyana cewar, shi ya umurci aikata kissan kiyasun ga mutanen Dujail, da a ka samu da hannu, a cikin kitsa makircin hallaka shi, a yayin da ya kai ziyara a wannan gari, a shekara ta 1982.