1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Tashin bom a Iraq

November 10, 2005
https://p.dw.com/p/BvLc

Mutane a kalla 30 ne suka rasa rayukan su a can kasar Iraqi sakamakon tashin wani bom a cikin wani gidan cin abinci a birnin Bagadaza. Ba a da bayan haka wasu mutanen da yawa ma sun samu raunuka iri daban daban.

A cewar wasu jami´i na kasar, dan kunar bakin waken ya tashin bom din ne jim kadan da shir sa a cikin otal din cin abincin dake tsakiyar birnin na Bagadaza.

Ya zuwa yanzu dai tuni kungiyyar Alqeeda dake da reshen ta a Iraqi tayi ikirarin cewa itace ta kai wannan hari na kunar bakin waken.

A waje daya kuma wasu bayanai da suka iso mana daga kasar ta iraqi na nuni da cewa wasu mutanen a kalla shida suma sun rasa rayukan nasu sakamakon tashin wani bom a kofar daukar ma´aikatar daukar sabbin soji dake yankin Tikirit