Tsagerun matasa a Ivory Coast sun kara kai wani sabon hari
January 19, 2006Talla
Tsagerun matasa magoya bayan shugaba Lauret Gabgbo sun kara kaiwa jami´an Mdd a birnin Abijan a kasar Ivory Coast hari.
Wannan dai hari na yau yazo ne a dai dai lokacin da kwamitin sulhu na Mdd ke tunanin kakabawa kasar takunkumi.
Tsagerun matasan dai sun ci gaba da gudanar da zanga zangar ne a rana ta hudu, duk kuwa da kiran da Shugaba Lauret Gbagbo na kasar da shugaba Obasanjo na Nigeria suka yi musu na daina tada zaune tsaye a kasar.
Kafin dai kai wannan hari , bayanai daga birnin sun nunar da cewa an bude wasu shaguna na saye da sayarwa a birnin to sai dai ba kamar yadda yake ada ba.