1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Tuhumar Kotu ta masu hannu a rikicin Jos

April 1, 2010

Wata Kotu a Jos ta tuhumi mutanen da ake zargi da ruruta wutan rikicin ƙabilanci na kwanakin baya a jihar Plateau.

https://p.dw.com/p/MlfV

Wata kotu a birnin Jos ta tuhumi mutane 20 da laifin ruruta wutan rikicin ƙabilanci na kwanakin baya, da ya haifar da salwantar rayukan ɗaruruwan mutane a Jihar Plateau. An ɗage zaɓen har i zuwa 15 ga wannan wata na Afrilu, bayan da ɗaukinsu suka ƙi amsa laifin da ake tuhumesu da aikatawa. Sai dai ana ganin cewa za a shafe watanni kafin a yanke hukuncin farko, sakamakon tafiyar hawainiya da harkokin shari´a suka saba yi a tarayyar ta Nigeria. Idan dai an same su da laifin da ake zarginsu da aikatawa, za a iya yanke musu hukuncin kisa.

Mutane 162 ke hannun jami´an tsaro a halin, amma kuma 41 daga cikinsu ne za a gurfanar gaban ƙuliya bisa zargin kisan kai da kuma aikin tarzoma. Ana ganin cewa hukumomin Nigeria na so su yi amfani da shari´ar wajen kawo ƙarshen jain ja da yana asalin Jos da kuma ƙabilar hausa-fulani ke yi.Rikicin na jihar Plateau da ya ƙi ci yaƙi cinyewa, ya sa tarayyar Nigeria ta yi ƙaurin suna a duniya a fiskar yakin ƙabilanci da kuma na addini.

Mawallafi: Mouhamadou Awal

Edita: Zainab Mohammed Abubakar