1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Turkiyya: Binciken harin ta'addanci a Ankara

Usman Shehu UsmanFebruary 18, 2016

Hukumomin kasar Turkiyya sun lashi takobin yin martani dangane da abun da suka ce harin ta'addanci a birnin Ankara, wanda ya yi sanadiyyar rayuka tare da raunata wasu.

https://p.dw.com/p/1Hx96
Türkei Anschlag in Ankara
Hoto: Reuters/U. Bektas

Akalla mutane 28 aka kashe a birnin Ankara na kasar Turkiyya lokacin da wata mota makare da bama-bamai ta yi bindiga lokacin da motocin bas na sojoji ke jiran denja ta ba su hanya a tsakiyar babban birnin kasar ta Turkiyya.

Ofishin gwamnan birnin ya ce an kai harin ne kusa da gine-ginen gwamnati da shalkwatar soji. Mukaddashin Firaminista Bekir Bozdag ya ce hari ne na ta'addanci.

A kuma halin da ake ciki Firaminista Ahmet Davutoglu ya soke tafiyar da so yi zuwa birnin Brussels. A wasu tagwayen hare-hare da aka kai birnin cikin watan Oktoban 2015 fiye da mutane 100 suka hallaka.