1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Wen Jiabao na ci gaba da ziyara a nahiyar Afrika

June 20, 2006
https://p.dw.com/p/But9

Praministan ƙasar Sin Wen Jiabao, na ci gaba da ziyara aiki a nahiyar Afrika.

Bayan ƙasashen Masar da Ghana, tun jiya ya fara rangadi a Congo, inda ya gana da shugaban ƙasar, bugu da ƙari shugaban ƙungiyar taraya Afrika Denis Sassou N´guesso.

A sakamakon wannan tantanawa,ƙasashen 2, sun rattaba hannu a kann yarjejeniyoyi daban-daban ta hanyar kasuwanci da kiwon lahia.

Sannan a yau, ya ziyarci babban asibitin Brazaville, kamin, ya sadu da ɗallibai na makarantar koyan halshen Sinanci dake ƙasar.

Nan gaba a yau Wen Jiabao, zai tashi zuwa Afrika ta kudu, inda bayan nhan zai ziyarci Angola da Tanzania