1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

WHO ta bukaci hadin kai don yaki da annoba

May 19, 2017

Kungiyar lafiya ta duniya WHO ta bukaci kasashe su kara himma wajen kare lafiyar jama'arsu daga barazanar annobar cutattuka.

https://p.dw.com/p/2dGtt
G20 Treffen der Arbeits- und Beschäftigungsminister Bad Neuenahr
Hoto: DW/M. Bierbach

Kungiyar lafiya ta duniya WHO ta bukaci kasashe su kara azama wajen kare lafiyar jama'arsu daga barazanar annobar cutattuka da kuma ka iya kaiwa ga haifar da koma bayan tattalin arziki.

Babbar daraktar kungiyar lafiyar ta duniya Margaret Chan ta baiyana haka a taron ministocin lafiya na kungiyar kasashe ashirin masu cigaban masana'antu na duniya G20 da ya gudana a birnin Berlin.

Ita ma da take tsokaci shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel kira ta yi ga kasashen masu ci gaban masana'antu su taimaka da kudade wajen samo sabbin hanyoyin yaki da annobar cutattuka.

Ta ce akwai bukatar mu kara kaimi yadda matakan da muke da su za su yi tasiri a nan gaba. Domin cimma wannan muna bukatar yin taka tsantsan wajen amfani da magungunan Antibiotics yadda kwayoyin cuttukan ba za su bijirewa maganin su cigaba da yaduwa cikin hanzari ba,