1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

WHO ta tabbatar da bullar kwalara a Kenya

July 22, 2017

Hukumar lafiya ta duniya WHO ta fito da wani gargadi kan alamun ta'asar cutar kwalara a kasar Kenya, sakamakon tabbatar da kasancewar kwayoyin cutar da ta yi.

https://p.dw.com/p/2gzz5
Bakterien Erreger der Cholera
Hoto: picture-alliance/Dr.Gary Gaugler/OKAPIA

Cikin wata sanarwar da ta yi dangane da lamarin, hukumar ta lafiya ta duniya ta ce ya zuwa yanzu ta tabbatar da kamuwar sama da mutum 300. Tuni ma dai cutar ta kwalara ta kashe mutane hudu a wasu manyan Otel-otel da ke Nairobi babban birnin kasar.

Hukumomin birnin sun dauki matakan bincike bayan samun akalla mutane 30 da suka kamu. An kuma fara tsananta binciken a wuraren saukar baki da kuma gidajen sayar da abinci. Ko a bara ma dai cutar ta kwalara ta kashe sama da mutane 200 a kasar yayin da wasu dubbai kuwa suka sha jinya.