1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ya kamata kasashen musulmi su kalubalanci na yamma

January 21, 2006
https://p.dw.com/p/BvBE

Shugaban Iran Mahmud Ahmedi-Nijad yayi kira ga kasashen musulmi da su yi amfani da karfin tattalin arzikinsu don tinkarar duk wani kalubale daga kasashen yamma. A jawabin da yayi a karshen ziyarar da ya kaiwa Syria shugaba Nijad ya ce kasashen musulmin ke da laifi idan suka taimakawa tattalin arzikin kasashen yamma. Shugaban ya ce ta haka suna ba wa´yan yamma damar yin amfani da karfi akan su. A dangane da takaddamar shirin nukiliyar kasar kuwa, ´yan siyasa a birnin Teheran sun yi gargadi game da wani sabon rikici a fannin samar da mai. A kuma halin da ake ciki mujallar Spiegel ta nan Jamus ta rawaito cewar hukumomin Iran sun gabatarwa ministan harkokin wajen Jamus Frank-Walter Steinmeier wata sabuwar shawarar game da warware rikicin nukiliyar.