Yajin aikin gama gari a kasar Habasha
November 8, 2005Talla
Yan adawa a kasar Habasha sun yi barazanar gudanar da yajin aiki na gama gari har tsawon mako guda domin nuna bacin rai ga abin da suka kira tabarbarewar alámura a kasar. An ruwaito cewa Kantuna a babban birnin kasar Addis Ababa sun kasance a rufe. Yan adawar na korafi a game da sakamakon zaben majalisun dokoki da aka gudanar a kasar a watan Mayun da gabata wanda suka ce an tafka magudi a cikin sa. A waje guda kuma gwamnatin ta kame wasu shugabanni ashirin da hudu na yan adawar ba tare da tuhuma ba.