1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Yaki da aiyyukan ta´adda a Masar

May 9, 2006
https://p.dw.com/p/Buz1

Yan sandan kasar Masar sun harbe shugaban kungiyyar tsagerun matasan da suka kai harin bam a yankin Sinai na yan yawon shakatawa.

A cewar rahotanni, yan sandan sun harbe Naseer Khamis Al Mallahi ne, bayan wani dauki ba dadi daya wanzu a tsakanin yan kungiyyar su ta Tawhid Wal Jihad da kuma jami´an tsaron.

Bugu da kari, jami´an tsaron sun kuma sami galabar cafke na hannun daman shugaban kungiyyar ta Tawhid wal Jihad, wato Mohd Abdalla Elian.

Idan dai za´a iya tunawa an zargi yan kungiyyar ta Tawhid wal Jidad din ne da kai harin bam a Dahab a watan afrilun daya gabata, wanda hakan yayi sanadiyyar rasuwar yan yawon shakatawa 19.