1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Yaki da cin hanci a Najeriya

Uwais Abubakar Idris | Abdourahamane Hassane
May 23, 2017

A karon farko mukadashin shugaban hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta Najeriya EFCC Ibrahim Magu ya jagoranci wani gagarumin gangami na wayar da kan jama’a a kan yaki da cin hanci da rashawa.

https://p.dw.com/p/2dRNI
Nigeria Plakate und Aufkleber gegen Korruption
Hoto: DW/K. Gänsler

Kokari na wayar da kan ‘yan Najeriya na su ankara daga tunanen cewar yaki da cin hanci aiki ne na gwamnati ita ka dai da hukumomin da ta kafa shi ne muhimmin sako da mukadashin shugaban hukumar Ibrahim Magu ya isar ga ‘yan Najeriya. Ko wane tasiri suke ganin wannan ganagmin zai yi ganin yadda sauran hukumomin tsaro da masu wayar da kan jama'a da yaki da cin hanci suka shiga gangamin na zaburar da ‘yan Najeriya su kara bude idno su don fafutukar masu halin bera a kasar. Bullo da tsari na tonon silili a harkar yakar masu nuna halin bera da ke yin sama da fadi da dukiyar al'umma a Najeriyar ya kara zaburar da al'ummar kasar sanin irin rawar da ya kamata su taka a kan wannan aiki. Masu gangamin sun bi ta gaban majalisar dokokin Najeriyar wacce ke takun saka a kan kin amincewa da mukadashin shugaban hukumar a takadammar da ake ci gaba da sa idon ganin yadda za ta kaya.