1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Yakin neman zabe a kasar Gabon

November 24, 2005
https://p.dw.com/p/BvJh

Ranar lahadi ce mai zuwa idan Allah ya kai mu, a ke shirya zaben shugaban kasa a Gabon.

A halin da ake ciki jam´iyu daban daban na ci kin yakin neman zabe, saidai masu kulla da a al`ammuran siyasar a kasar sun tabbatar da cewa, babu shaka Shugaba Omar Bango za shi tazarce a wannan mukami.

Omar Bango na da shekaru 28 daidai bisa karagar mulkin kasar Gabon, idan a ka zabe sa ranar 27 ga watan nobemba, zai kara wasu shekaru 7.

Jam´iyun adawa sun zargi shugaban kasar, da anfani da dukiyar jama´a, a cikin yakin neman zabe.

Kamar yadda dokoki su ka tanada a Gabon, zagaye daya kawai a keyi a zaben shugaban kasa, matakin da ke kara tabatar da shugaba mai ci yanzu za shi tazarce.