'Yan adawa sun ƙauracewa zaɓen Burundi
June 28, 2010Talla
'Yan takara shida na jam'iyun adawa sun ƙauracewa zaɓen shugaban ƙasa da aka fara yau litinin a Burundi. Wannan janyewar da 'yan adawa sukayi ya sa shugaba mai ci Pierre Nkurunziza ya zama ɗan takara ɗaya tilo.
Janyewar 'yan takarar ya biyo bayan zargin tafka maguɗi ne a zaɓen ƙananan hukumomin da aka gudanar a watan mayun bana.
Kanfanin dillancin labaran jamus ta ruwaito ƙungiyar cigaban ƙasashen tsakiyar afirka data ƙunshi ƙasashen Tanzaniya da Uganda da Kenya da kuma Rwandan sukayi gargaɗin samun tashin hankali a wannan zaɓe.
Shekaru 45 da samun 'yancin kai, ƙasar ta samu kanta cikin yaƙin basasa, bayan shugabannin ta uku da aka kashe.
Mawallafi: Babangida Jibril
Edita: Mohammad Nasir Awal