1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

'Yan adawa za su kalubalanci Yahya Jammeh

October 31, 2016

A Gambiya Hadin gwiwar kungiyoyin 'yan adawa sun zabi dan takara daya lak tilo wanda zai kalubalanci shugaba Yahya Jammey a zaben shugaban kasa.

https://p.dw.com/p/2RxkC
Elfenbeinküste Präsident Yahya Jammeh in Yamoussoukro
Hoto: Getty Images/AFP/I. Sanogo

Adama Barrow dan shekaru 51 jagoran jam'iyyar UDP shi ne hadin gwiwar jam'iyyun siyasar na adawa guda bakwai suka wakilta ya tsaya takara a zaben na watan Disamba da ke tafe,wanda shi ne karo na biyar ke'nan da Yahya Jammey zai yi takara.Jammeh wanda ya zo kan karagar mulki bayan wani juyin mulkin a shekara ta 1994  kafin ya rikide ya koma farar hula kungiyoyi  masu fafutuka  da na 'yan adawar kasar da kuma 'yan jaridu na zarginsa da take hakin bil Adama.