1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

yan majalisar dattijai na Amurka sun datse hanyoyin muhawara kan Iraki

February 6, 2007
https://p.dw.com/p/BuSJ

ISRAEL CONSTRUCTION

Mahukuntan kasar Israila sun fara share wani yankin kasa a wajen tsohon birnin Urushlima inda ake gardaman wurin ibadan nan na Temple mount da Harem al-Sharif,tsakanin yahudawa da musulmi a wannan yankin.

Shugabanin palasdinawa sun yi kira ga dukan musulman yankin da su fito su kare Israila da rusa wannan muhimmin wurin ibada.An bayyana cewa ana gudanar da aikin ne karkashin cikakken tsaro na daruruwan yan sanda.

STRIKE KASHMIR

An tsare wasu yan zanga zanga da ke nuwa rashin amincewan su game da kisan kiyashin da yan sanda suka yi wa alumman faran hula a kashmir.

Daruruwan mutane maza da mata ne suka fito zangazangar suna Ihu suna ta wake wake .

Inda Wasu suka yi ta jefa duwatsu way an sandan yayin garkuwa da su,daga bisani ne dai yan sandan suka jefa barkonon tsohuwa way an zangazangan.Ba abayyana sanin ila a sakamakon haka ba tukuna.