1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Shari'a tsakanin 'yan Najeriya da Shell

Yusuf BalaDecember 18, 2015

Mai shari'a Hans van der Klooster ya ce kotun daukaka karar da ke a birnin Hague na da hurumi na sauraran wannan shari'a.

https://p.dw.com/p/1HPwq
Umweltverschmutzung im Niger Delta
Yankin da hakar ma'adanai ta gurbata a Niger Delta-NajeriyaHoto: picture alliance/AP Photo

Wata kotun daukaka kara a kasar Holand ta bayyana a ranar Juma'an nan cewa wasu manoma hudu 'yan Najeriya na da dama a kasar su daukaka karar da suke yi ta kamfanin hakar albarkatun man fetir wato Shell cewa ya bata musu muhalli a Najeriya. Wannan hukunci dai na zama wanda ya kafa tarihi da aka samu hannun kamfanin na Shell a irin wannan shari'a.

Mai shari'a Hans van der Klooster ya ce kotun daukaka karar da ke a birnin Hague na da hurumi na sauraran wannan shari'a kan kamfanin da ke da reshe a Najeriya.

Manoman hudu da masunta daga yankin Niger Delta a Najeriya sun sami goyon baya ne na wata kungiya mai fafutikar kare muhalli mai suna Freands of the Earth wacce tun a shekarar 2008 ta gurfanar da wannan kamfani a kotun da ke da tazarar dubban kilomitoci daga inda lamarin gurbata muhallin ya faru.