1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

'Yan sanda a Togo sun kashe masu zanga-zanga

August 20, 2017

Jami'an 'yan sanda a Lome babban birnin kasar Togo, sun buda wuta a kan masu zanga-zanga inda suka halaka biyu daga cikinsu, wasu 13 kuwa suka ji rauni, yayin wani boren da suka yi a jiya Asabar.

https://p.dw.com/p/2iWBA
Ausschreitungen in Lome Togo
Hoto: Reuters

Jami'an 'yan sanda a Lome babban birnin kasar Togo, sun buda wuta a kan masu zanga-zanga inda suka halaka biyu biyu daga cikinsu, wasu 13 kuwa suka ji rauni, yayin wani boren da suka yi a jiya Asabar. Mutanen dai na zanga-zangar nuna adawa ne da mulkin zuria'ar Gnassimbe na kasar.

Shugaba Faure Gnassimbe da ke kan karaga, na mulki ne tun a shekara ta 2005 bayan mutuwar mahaifinsa Gnassimbe Eyadema da ya mulki kasar tsawon shekaru 38. Dubban jama'a ne dai suka yi zanga-zangar a Lome, suna mai cewa shekaru 50 mutane daya ke mulkin, ya yi yawa, suna mai kiran yin gyara ga tsarin mulki ta yadda zai takaita wa'adin mulki.