1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

'Yan sandan Kenya sun binge mutum uku

Abdul-raheem Hassan
November 17, 2017

An harba hayaki mai sa hawaye kan ayarin madugun adawar kasar Raila Odinga yayin da ya ke shiga kasar daga tafiyar da ya yi, sannan an bude wuta kan magoya mayan sa da ke hidimar tarbar sa a babban birnin kasar Nairobi.

https://p.dw.com/p/2np9Z
Kenia Wahlen - Ausschreitungen in Nairobi
Hoto: Reuters/G. Tomasevic

Kashe 'yan adawar uku na zuwa ne bayan da 'yan sanda suka ce suna yunkurin kwantar da zanga-zangar da magoya bayan Odinga ke yi, kamfanin dillancin labarun Faransa AFP ya ce, 'yan sanda sun fetsa ruwan zafi da hayaki mai sa hawaye kan ayarin madugun adawa, abin da ya hargitsa magoya bayansa yin martanin jifa da duwatsu kan jami'an 'yan sandan.

Kasar Kenya dai na cikin rudanin siyasa tun bayan da kotun koli ta soke sakamakon zagayen farko na zaben shugaban kasar da aka gudanar a watan Agusta, to sai dai da alamu tsugune bata kare ba, inda ake san ranar Litinin mai zuwa kotun koli za ta yanke hukunci kan ko za a rantsar da shugaba Uhuru Kenyata a mastayin shugaba karo na biyu ko za a sake zaben.