Yan tawaye sun fafata da dakarun Chadi
November 25, 2006Talla
Dakarun gwamnati a kasar Chadi sun fafata da yan tawaye a kusa da garin Abeche dake gabashin kasar.
Maaikatan agajai a Abeche sunce sunji karar harbin bindigogi a wajen birnin.
Yan tawaye dai sun kara kaimin hare hare da suke kaiwa cikin yan watannin nan a kokarinsu na hambarar da gwamnatin Idriss Deby.
Gwamnatin dai ta zargi kasar Sudan da laifin baiwa yan tawayen taimako,wanda kuma tuni Sudan din ta karyata.
A jiya jumaa ne kuma gwamnatin Chadi ta kara waadin watannin 6 kann dokar ta bacin da ta kafa a ranar 13 ga watan nuwamba a N’djamena da wasu yankuna ciki har da gabashin kasar.