1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Yarjejeniyar sulhu tsakanin gwamnatin Sudan da ´yan tawayen JEM.

February 24, 2010

An cimma yarjejeniya a birnin Doha tsakanin gwamnatin Sudan da ´yan tawayen JEM

https://p.dw.com/p/M9kb
`Yan tawayen JEM na Sudan sun ajje makamaiHoto: picture-alliance/dpa
Gwamnatin Sudan ta rattaba hannu kan yarjejeniya tare da ƙungiyar ´yan tawayen Justice and Quality Movement wato JEM a ɓirnin Doha. Wannan yarjejeniya za ta bai wa ƙungiyar ´yan tawayen damar raba madafun iko  da gwamnati. Doka ta ukku da wannan yarjejeniya ta ƙunsa ta nunar da cewa gwamnatin Sudan da yan tawayen  JEM sun yarda a dama da ƙungiyar yan tawayen ta JEM a dukan matsayi na iko. Sai dai wannan yarjejeniya ta nunar da cewa a nan gaba ne bangarorin biyu za su amince da wannan doka da aka rattaba hannu a kanta a Doha, babban ɓirnin Katar. A bayanin da Anja Dargatz, wakiliyar asusun Friedrich Ebert da ke ɓirnin Khartum game da yarjejeniyar cewa ta yi da farko wajibi ne mu yi bayani cewar ba maganar wata yarjejeniya ce ta zaman lafiya ba, sai domin a albarkaci wata yarjejeniya ce ta ajiye makamai, wadda aka cimma daidaituwa kanta a Chadi ranar asabar da ta wuce, wadda kuma a yanzu aka ɗaga matsayinta zuwa rukunin shawarwarin sulhu na Doha. JEM dai ta yi nuni da cewar wannan wani mataki ne na farko game da kwance damarar makamai, amma kuma dole ne gwamnati ta nuna alkiblar da ta fuskanta. A saboda haka gaba daya magana ce ta neman kusantar juna tsakanin sassan biyu, amma ba wata yarjejeniya ce ta zaman lafiya ba. Dokar dai ta buƙaci ɓangarorin biyu da su amince da JEM a matsayinta na babbar ƙungiyar 'yan tawaye a Sudan da ta cenja zuwa jam´iyar siyasa. Wadda ke nan ƙungiyar ta JEM za ta kasance jamiyar siyasa da zaran an rattaba hannu a kan kamalalliyar yarjejeniyar nan ta ranar 15 ga watan Maris mai zuwa kafin zaɓen da zai gudana a ƙasar ta Sudan a watan Afrilu ,wanda shi ne zaɓe irinsa na farko cikin shekaru 24 da suka gabata. A  ranar asabar da ta gabata sai da wakilan gwamnatin Sudan da na yan tawayen suka sa hannu a kan daftarin wannan doka a ƙasar Chadi suna masu shelar tsagaita buɗe wuta a rikicin lardin Darfur da aka shafe shekaru bakwai ana fuskanta. Sun kuma yarda su kadammar da tattaunawar gaggawa domin cimma yarjejeniyar  da kuma haɗe mayakan JEM da sojoji da yan sandan ƙasar ta Sudan. Shugaban Sudan Omar Hassan Albashir ya je ɓirin Doha tare da shugaban JEM Kamal Ibrahim. Shugaba Idris Deby na Chadi da sarkin Katar Sheikh Hamad Bin Khalifa al-Thani wanda ƙasarsa ta ɗauki dawainiyar gudanar da tattaunawa tsakanin gwamnatin Sudan da yan tawayen su kuma sun halarci wannan taro. Ko kafin shiga wannan taro Shugaba Albashir ya yi jawabi inda ya kira yarjejeniyar ta zaman lafiya tamkar matakin farko na kawo ƙarshen rikicin lardin Darfur tare da kyautata fatan cewa za a cimma kyakkyawar yarjejeniya a wannan lardi na yammacin Sudan kafin gudanar da zaɓe. A  cewar Majalisar Ɗinkin Duniya, mutane dubu ɗari ukku suka rasa rayukansu a rikicin na yankin Darfur a baya ga wasu su miliyan biyu da ɗari bakwai da suka rasa matsugunansu. Mawallafi: Hussaina Jibril Yakuba Edita.: Ahmed Tijani Lawal