1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Yawan wadanda suka mutu a wata gobara a China ya karu

Mohammad Nasiru AwalAugust 13, 2015

Mahukunta a birnin Tianjin sun ce fashewar abubuwa da kuma gagarumar gobara da ta tashi ta kuma haddasa babbar asara.

https://p.dw.com/p/1GFIn
China Explosion in Hafenstadt Tianjin
Hoto: Reuters/China Daily

An tabbatar da mutuwar akalla mutane 50 sannan 701 sun samu raunuka, 71 raunuka masu tsanani a fashewar wasu abubuwa a birnin Tianjin mai tashar jirgin ruwa a kasar China. Mahukunta a birnin sun ce fashewar abubuwa da kuma gagarumar gobara da ta tashin ta kuma haddasa babbar asara. Wani faifayen bidiyo ya nuna yadda harshen wuta ya mamaye sararin samaniyar birnin.

A ranar Laraba da dare an kira 'yan kwana-kwana lokacin da gobara ta tashi a wani wurin ajiye kaya da suka hada da sinadarai masu guba a tashar jirgin ruwa. Amma sai kwatsam wasu abubuwa masu yawa suka fara fashewar lokacin da masu kashe gobarar suka isa wurin, sun kuma rasa akalla ma'aikatansu su 12.