1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Zaɓe a Timor ta gabas

April 9, 2007
https://p.dw.com/p/BuNy

Yau ne al´ummomin yankin gabacinTimor, su ka shirya zaɓen shugaban ƙasa.

Rahotani daga ƙasar sun nunar da cewa, mutane masu yawa sun kaɗa ƙuri´a, sannan an gudanar da zaɓen lami lahia duk ruɗani da fargaba da ke zukatan jama´a,kamar yadda Praministan ƙasar Jose Ramos-Horta yayi hasashe kamin fara zaɓen.

Saidai Hukumar zaɓe mai kanta ta ƙasa, ta koka da ƙaranci takardun zaɓe, to amma a cikin ɗan lokaci ƙanƙane jiragen sama masu dura angulu, na Majalisar Ɗinkin Dunia su ka magance wannan matsala.

Wannan shine zaɓen farko, da al´ummomin ƙasar su ka yi, tun bayan samun yancin kanta, a shekara ta 2002.

Shugaban mai ci y