1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Zaɓen ƙasar Gini

June 28, 2010

An bayyana zaɓen ƙasar Gini da cewa an yi adalci

https://p.dw.com/p/O4lp
Masu kaɗa ƙuri'a a Gini suna jira a layi domin jefa ƙuri'arsuHoto: AP

Masu sa ido a zaɓen ƙasar Gini da ya gudana a ranar Lahadi, sun kwatanta zaɓen na Konakry a matsayin wanda ya gudana cikin adalci. Masu sa idon daga ƙungiyar Tarayyar Turai da Tarayyar Afirka haɗe da ƙungiyar haɓaka tattalin arzkin ƙasashen Afirka Ta Yamma wato ECOWAS duk sun yaba da zaɓen, wanda shi ne zaɓen shugaban ƙasar Gini na farko, da babu hannun soji tun samun 'yancin ƙasar a shekara ta 1958. An bayyana samun fitowar ɗimbin masu kaɗa ƙuri'a a ƙasar dake yammacin Afirka. Ana dai sa ran kaiwa zagaye na biyu a watan gobe, domin bisa dukkan alamu babu wanda zai samu nasara kai tsaye. Izuwa jibi ne dai ake sa ran samun sakamakon zaɓen daga hukuma.

Mawallafi: Usman Shehu Usman

Edita: Mohammad Nasiru Awal