Zaɓen gama gari a Belgium
June 13, 2010A yau ake gudanar da zaɓen gama gari a ƙasar Belgium. Masu zaɓe za su yanke hukunci akan makomar wannan ƙaramar ƙasa wadda al'ummar ta masu magana da harshen Dutch miliyan 6.5 da masu magana da harshen Faransanci miliyan huɗu ke nuna rashin jin daɗinsu ga zaman tarayya. Ana sa ran cewa babbar jam'iyar 'yan Flemish dake neman ɓallewa tare da 'yan Dutch zuwa tarayyar Turai, za ta taka rawar gani. Har in ta faru to hakan na nufin babban koma-baya ga 'yan Wallonia wato al'ummar kudancin Belgium masu magana da harshen Faransanci, waɗanda talakawa ne da suka dogara kan tallafi daga yankin 'yan Flemish. An dai kira wannan zaɓe na gaba da wa'adi ne bayan rushewar jam'iyar ƙawance ta Firaminista Yves Leterme a cikin watan Afrilu sakamakon wata taƙaddama game da wata mazaɓa ta masu amfani da harsuna guda biyu.
Mawallafi: Mohammad Nasiru Awal
Edita: Yahouza Sadissou Madobi