1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Za´a ci-gaba da gangami har sai an ga bayan gwamnatin Libanon

December 8, 2006
https://p.dw.com/p/BuYp
Shugaban kungiyar Hisbollah Sheikh Hassan Nasrallah ya fadawa dubban magoya bayan sa cewar sannu a hankali zasu kifar da gwamnatin Libanon mai samun daurin gindin kasashen yamma. Wannan sanarwa ta shugaban na Hisbollah ta zo bayan kwanaki 7 na zanga-zangar da kungiyar ta Hisbollah da masu goyon bayan Syria suka shirya da zummar kayad da gwamnatin FM Fuad Siniora. A cikin wani jawabi Nasrallah ya zargi FM Siniora da hada baki da Isra´ila a lokacin yakin nan na wata daya da Hisbollah ta yi da da kasar Yahudun Isra´ila. Ya ce FM ne ya umarci sojojin Libanon da su kwace makaman Hisbollah.