1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Zaben shugaban kasa a Tajikistan

November 6, 2006
https://p.dw.com/p/Bud8

Alummomin kasar Tajikistan nacigaba da yin dafifi zuwa cibiyoyin zabe domin kada kuriunsu a zaben shugaban kasa,zaben da ake ganin cewa Shugaba Emomali Rakhmonov na yanzu ,zai sake samun nasarar komawa madafan iko.Rahotanni daga kasar dai na nuni dacewa sama da kashi 65 daga cikin 100,na masu zaben kasar sun rigaya sun kada kuriun su,a saoi shida na farkon ranar zaben na yau.To sai dai tuni shugaba Rakhmonov yayi watsi da kalaman sukan daga masu gani da ido na kasashen turai ,akan tsarin yadda zaben ke gudana.Ya hakikance cewa zaben na gudana ne bisa tafarkin Democradiyya,sai dai ya gaza tsarin na kasashen turan.