1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Zaben ´yan majalisar dattijan Zimbabwe

November 26, 2005
https://p.dw.com/p/BvJS

A yau al´umar kasar Zimbabwe ke kada kuri´a a zaben ´yan majalisar dattawar kasar. To sai dai ana ganin zaben tamkar wani wasan yara wanda ke da nufin karfafa ikon da jam´iyar shugaba Robert Mugabe ke da shi akan ´yan majalisun dokokin kasar. Masu sa ido a zabe sun yi hasashen cewa mutane ba zasu fita sosai don kada kuri´a ba musamman a daidai lokacin da ake kara saka ayar tambaya dangane da rawar da wannan majalisa mai wakilai 66 zata taka. Zaben ya kuma janyo rarrabuwar kawuna a tsakanin jam´iyar adawa ta MDC game da kauracewa zabe ko a´a.