1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Zanga-zanga a Afirka ta Kudu

Abdourahamane Hassane
April 12, 2017

Dubban jama'a a birnin Pretoria na Afirka ta Kudu sun pantsama a kan tituna, a zanga-zangar da 'yan adawar suka kira domin tilasta wa shugaba Jacob Zuma da ya yi marabus daga kan karagar mulki.

https://p.dw.com/p/2b80J
Protest gegen Zuma in Pretoria
Hoto: Reuters/S.Sibeko

Hakan kuwa na zuwa ne gabannin zaman majalisar dokokin kasar wacce za ta ka'da kuri'ar yanka kauna ga shugaban kasar.Shugaba Jacob Zuma wanda ake zargi da laifin cin hancin na fuskantar bore a 'yan kwanakin baya-baya nan, tun bayan da ya yi wa majalisar ministocinsa gyaran fuska wadda a ciki ya salami minitan kudin kasar Pravin Gordhan.