1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Zanga-zanga a kasashen musulmi

February 7, 2006
https://p.dw.com/p/Bv8y

A kasashe daban daban na musulmi a na ci gaba da zanga zangar nuna bacin rai , bayan tozarci da wata jaridar Danmerk ta yi wa Manzan Rahama,ta hanyar zana hotuna, masu suppanta shi da,dan ta´ada.

A Iran bayan zanga zamngar jiya a yau ma dubunan jama´a ne su ka yi cincinrido, a opishin jikadancin Danmark, dake birnin Teheran, saidai Jami´an tsaro su hanna su, kone wannan opishi.

Idan ba a manta ba, kasar Iran, ta bayyana katse duk wasu huldodin cinikayya da Danmerk, domin nuna fushi ga wannan aika aika, da jaridar ta yi.

Kazalika, a birane da dama na kasar Indonisia, masu zanga zangar, sun ci gaba da kone tutocin Danmark.

Hukumomin wannan kasa , sun yi kira ga al´ ummomin su, da ke zaune a Indonesia, Iran Labanon, da Syria da su

Gaggauta fita daga wannan kasashe.