1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Zanga-zanga a Moroko

January 29, 2017

Dubban mutane suka yi zanga-zanga domin ganin an dauki mataki kan yaki da cin hanci da kuma kyautata aikin malaman makarantu.

https://p.dw.com/p/2WbE0
Marokko | Proteste in Rabat
Hoto: Getty Images/AFP/F. Senna

Dubban 'yan kasar Moroko ne suka yi zanga-zangar adawa da gwamnati, inda suke neman sai a dau matakan yaki da cin hanci, kana a kyautata aikin malaman makarantu. Kimanin kungiyoyin kwadago 1000 suka kira magoya bayansu domin shiga zanga-zangar da aka yi Rabat babban birnin kasar ta Moroko.

Bayaga kungiyoyi kwadago, wasu 'yan jam'iyyun adawa da masu fafitikar kare hakkin jama'a sun shiga zanga-zangar. Daga bisani wasu malaman makaranta kimanin 2000 suka yi dafifi a gaban majalisar dokoki, inda suke cewa dole a soke ayar doka wace ta rage almabashinsu.