1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Zargin cin hanci a Venezuela

Gazali Abdou Tasawa
August 24, 2017

Tsofuwar alkalin alkalai ta kasar Venezuela wacce ta yi hijira zuwa Braziliya Luisa Ortega ta ce tana rike da bayyanai da dama da kuma hujjoji na cin hancin da karpar rashawa da Shugaba Nicolas Maduro yake yi.

https://p.dw.com/p/2ijX4
Venezuela - Generalstaatsanwältin Luisa Ortega Diaz leistet weiterhin Widerstand
Hoto: Getty Images/AFP/L. Robayo

Luisa Ortega  wacce ta isa Brazil  daga Kwalambiya ta sheda wa wani taro alkalai na kungiyar kasashen yankin Latine Amirka cewar  Nicolas Maduro  na hada baki da 'yan uwansa don satar kudi kasar. Ta kuma ce sun gano dalla biliyan 100 da sghuban ya sace,wani dan uwansa ya kai ya ajiye a Spain.