1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Zimbabwe ta kira Jakadanta na Jamus gida

Ibrahim SaniDecember 11, 2007
https://p.dw.com/p/CaG0

Jamus ta soki ƙasar Zimbabwe da kakkausan harshe, game da baƙaƙen maganganun da aka kira shugabar Gwamnatin Jamus da su. Hukumomin na Berlin sun ce hakan abune da ka iya lalata dangantakar dake akwai a tsakanin ƙasashen biyu. A jiya ne ministan yaɗa labarai na Zimbabwe, Sikhanyiso Ndlova ya zargi

Shugaba Merkel da cewa shugaba ce mai nu na wariyar launin fata.

Rahotanni sun ce tuni Zimbabwe ta kira jakadanta na Jamus izuwa gida, don nuna adawa da kalaman shugabar Gwamnatin kan ƙasar. A lokacin da take jawabi a taron ƙolin birnin Lisbon tsakanin Nahiyar Afrika da Turai, Merkel ta soki lamirin Zimbabwe da take hakkoki na bil adama. Merkel ta kuma ƙara da cewa matakin abune dake rage ƙimar Nahiyar ta Afrika a idon Duniya.