Ziyara Jan Egeland a kasar Zimbabwe
December 5, 2005Talla
Shugaban hukumar bada agaji ta Majalisar Dinkin Dunia ya kai ziyara gani da ido a kasar Zimbabwe.
A yayin da ya ziyarci yankunan da gwamnati ta ruguza gidajen talakawa, a watannin da su ka wuce, Jan Egeland ya nuna matukar taikaici da taussayi.
Ya bayyana mayuyacin halin talauci, da karancin abinci da tabarbarewar kiwan lahia,da al´umma ke ciki a wannan yanki.
Shugaban yayi kira ga kasashe dunia da kungiyin agaji na kasa da kasa da su ceci rayukan jama´ar da ke zaune a yankin.
Da farko gwamnatin Zimbabwe ta dauki matakin kin amincewa da karbar taimako zuwa ga mutanen, kamin daga bisani ta amince.