ziyarar kwanaki uku da Mr Egeland keyi a Ivory Coast
February 16, 2006Talla
A wani lokaci ne a nan gaba kadan a yau ake sa ran shugaban hukumar bayar da tallafin gaggawa na Mdd, wato Mr Jan Egeland zai kai ziyara izuwa garin Guiglo dake yammacin kasar Koddebuwa.
Kafin dai wannan ziyara, a jiya Mr Egeland ya bukaci gwamnatin kasar data dauki matakin kwancewa yan tawayen kasar damara, a
hannu daya kuma da zakulo wadanda suka kaiwa jami´an hukumar da dakarun sojin kiyaye zaman lafiya hari a watan daya gabata don hukunta su.
Mr Egeland , wanda ya isa kasar ta Kuddebuwa a ranar talata, na gudanar da ziyarar aiki ne ta tsawon kwanaki uku.
A wata sabuwa kuma Mdd ta aike da karin sojin kiyaye zaman lafiya zambar 200 izuwa kasar don bunkasa harkokin tsaro ga kayayyakin majalisar dake kasar ta Ivory Coast.