1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ziyarar Merkel a yankin gabas ta tsakiya

April 1, 2007
https://p.dw.com/p/BuOS

Shugabar gwamnatin jamus Angela Merkel ta gana da shugaban yankin palasdinawa Mahmoud Abbas a birnin Ramallah.Merkel ta fadawa yan jarida cewa akwai tabbacin cewa zaa sake farfado da tattaunawar samarda zaman lafiya tsakanin palasdinu da Izraela.

Ta bayyana cewa burinsu a nahiyar turai shine a samu zaman lafiya tsakanin wadannan bangarori guda biyu na yankin gabas ta tsakiya,kuma zasu bada dukkan goyon bayansu domin ganin an cimma hakan.

Angela Merkel wadda ke ziyarrata ta farko a wannan yanki a matsayin shugabar kungiyar tarayyar turai ,ta bayyana cewa cimma sasansanta bangarorin biyu,zai taimaka matuka gaya wajen samarwa palasdinu yantacciyar kasa ,kusa da izraela.