1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ƙungiyar AU ta gargaɗi Sudan da Sudan ta Kudu da su tattauna

December 15, 2012

AU ta ce ya zama dole ta yi amfani da ƙudirinta domin shirya zaɓen raba gardama a yanki Abyei, inda ƙasashen biyu sun kasa samu daidaito tsakanin su

https://p.dw.com/p/1737Y
General picture of an ECOWAS Summit gathering west African leaders to plot a military strategy to wrest control of northern Mali from Islamist groups as fears grow over the risks they pose to the region and beyond, on November 11, 2012 in Abuja. West African plans could see the mobilisation of some 5,500 soldiers, essentially but not totally drawn from the region. Between 200 and 400 European soldiers will train troops in Mali, according to the operational plan. AFP PHOTO / PIUS UTOMI EKPEI (Photo credit should read PIUS UTOMI EKPEI/AFP/Getty Images)
Hoto: PIUS UTOMI EKPEI/AFP/Getty Images

Ƙungiyar haɗin kan ƙasashen Afirka ta yi kiran da a gaggauta sake koma kan tebrin shawarwari tsakanin Sudan da Sudan ta kudu,akan taƙddamar da suke yi akan yanki nan mai arzikin man fetir na Abyei da ke tsakanin ƙasashen biyu.

Tattaunawa da nufin samun sulhu tsakanin sasan biyu ita ce za ta tantance makomar yankin wanda har yanzu bai san tudun dafawa ba.Wani kwamitin tsaro na ƙungiyar da ke shiga tsakanin ƙasashen biyu wanda suka dakatar da yaƙi a watannin da suka gabata, ya bai wa hukumomin Khartum da na Juba wa'adin ranar biyar ga wannan wata na su sasanta sai dai, lokacin har ya zo ya wucce ba tare da a ɗimke ɓarakar. Ƙungiyar ta haɗin kan ƙasashen Afirka ta yi gargaɗin cewar akan rashin ɗasawa da aka gaza cimma tsakanin ƙasashen biyu to kam su zasu ɗauki mataki.

Mawallafi : Abdourahamane Hassane
Edita : Saleh Umar Saleh