1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ƙungiyar EU za ta tallafa wa Girka

Abdourahamane HassaneMarch 20, 2015

Firaministan Girka Alexis Tsipras ya tattauna da shugabannin ƙasashen Jamus da Faransa da kuma hukumomin kuɗi na EU.

https://p.dw.com/p/1EuKg
Brüssel Alexis Tsipras
Hoto: picture-alliance/dpa/S. Lecocq

Ƙasashen dai na Ƙungiyar Tarrayar Turai sun yi alƙawarin tallafa wa ƙasar ta Girka da kuɗaɗen rance domin kiyayeta ga talauci tun da ga watan gobe.Amma bisa sharaɗin ƙaddamar da shirin tsuke bakin aljihun gwamnatin gabannin samun rancen na biliyan bakwai.

A share ɗaya kuma taron na Brussels ya sanar a cewar takunkumin karya tatalin arzikin da ƙasashen suka ƙaƙabawa Rasha.Zai ci gaba da kasancewa har sai yarjejeniya zaman lafiyar da aka cimma a gabashin Ukraine ta tabbata.