1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ƙungiyar NATO na gudanar da taro a birnin Brussels

April 1, 2014

Ministocin harkokin waje na Ƙasashe 28 membobi a Ƙungiyar Tsaro ta NATO, zasu gudanar da wani zaman taro kan batun ƙasar Yukren.

https://p.dw.com/p/1BZP3
Hoto: Getty Images

A wannan Talatar ce (01.04.2014) Ministocini zasu duba yiyuwar ƙara karfin ƙungiyar tsaron ta NATO a yankin Turai ta Gabas. Inda kuma a wannan rana ce NATO za ta fara wani sabon attisaye, na sa ido kan sararin samaniya a yankin Vilnuis, attisayan da zai samu halartar jiragen yaƙi na turai da Amirka. A hannu ɗaya kuma shugabannin diplomasiyar ƙasashen Jamus, Faransa, zasu yi wani zaman taro a dabra da taron ministocin harkokin wajan membobi a ƙungiyar NATO.

Daga na shi ɓangaren yau ne ake sa ran kamfanin nan, mai Fitar da iskar Gaz na ƙasar Rasha, zai tsawala kuɗin Gaz ga ƙasar ta Yukren.

Mawallafi: Salissou Boukari
Edita : Abdourahamane Hassane