1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

A Burkina Faso an yi jana'izar mazajen da suka fadi a fagen dagga

Abdourahamane HassaneDecember 2, 2014

Dubban jama'a tare da hukumomi sun gudanar da jana'izar mazajen da suka mutu a lokacin zanga-zagar da ta share gwamnatin Blaise Compaore.

https://p.dw.com/p/1DyNl
Burkina Faso neue Regierung in Ouagadougou Gruppenfoto
Hoto: STR/AFP/Getty Images

Jama'ar waɗanda suke riƙe da juna hannu da hanu a ciki har'da shugaban gwamnatin riƙon ƙwaryar Michel Kafando tare da fira ministan Lt. Col. Isaac Zida.Sun taru a wani dandali da aka sake farfaɗo da sunansa tun lokacin mulkin Thomas Sankara wato danalin juyin juya hali.

Inda daga can ne aka ɗauki gawarwakin mamanta a cikin wata motar soji zuwa maƙabarta.Mutane 24 suka mutu a zanga-zangar da aka yi a ƙarshen watan Oktoban jiya a ƙasar ta Burkina Faso