1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

A Najeriya mazauna Garkida na neman dauki

February 22, 2020

Bayan hari da 'yan bindiga suka kai garin Garkida da ke karamar hukumar Gombi a jihar Adamawa ta Najeriya, har yanzu ana cikin zulumi gami da neman dauki na tsaro.

https://p.dw.com/p/3YBkm
Boko Haram
Hoto: Java

Mazaunan a garin na Garkida sun tabbatar da kone-kone da 'yan bindigar da ake zargin na Boko Haram ne suka yi ciki har da majami'u da gidajen fitattun 'ya'yan yankin.

Rahotanni na cewa mazauna garin na Garkida na cikin hali na dar-dar, bayan harin da 'yan bindiga suka kansu a ranar Juma'a.

Wani mazaunin garin, Manu Usman Bakari, wanda a ya tsare da iyalinsa, ya yi wa DW bayani tare da tabbatar da mutuwar wasu jami'an tsaro.

Galibin jamaa dai sun kaurace wa garin, saboda fargabar abin da ka yia kasancewa. An kuma kokawa kan rashin kasuwanni da shagunan sayar da magunguna.