1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

A wannan Alhamis din ce ake hawan Arfa

October 25, 2012

Yau Alhamis ce tara ga watan Zul-Hijja al'ummar musulmi da su ka samu sukunin yin aikin hajjin bana ke yin hawan Arfa, a filin Arfa da ke wajen birnin Makkah.

https://p.dw.com/p/16W2s
epa02992433 Muslim pilgrims perform Friday prayer around the holy Kaaba in the center of the Haram Sharif Great Mosque, on the first day of the Muslim's Haj 2011 pilgrimage, in Mecca, Saudi Arabia, 04 November 2011. According to the Muslims holly book the Quran, the Kaaba was built by Abraham and his son Ismael, after Ismael had settled in Arabia. Millions of Muslims arrived in Saudi Arabia to perform their Hajj. The Hajj 2011 is due to take place from 04 to 09 November. EPA/AMEL PAIN
Haddsch PilgerfahrtHoto: picture-alliance/dpa

Tun a jiya Laraba ce dai maniyata aikin hajjin na bana sanye da harami su ka fara fita zuwa Muna inda za su share akasarin yau su na gudanar da ibada a filin na Arfa wanda shi ne kololuwa na aikin hajji.

Hukumomin Saudiyya dai sun ce kimanin mutane miliyan biyu da rabi ne za su gudanar da aikin hajjin na bana wanda miliyan daya da dubu dari bakwai su ka fito daga ƙasashen duniya daban-daban.

Saudiyyan dai ta ce ta yi kyakkyawan shiri da nufin bawa mahajjata damar yin aikin cikin kwanciyar hankali da kuma yanyi na tsafta da kyakkyawan tsaro gami da ɗaukar matakai na kula da lafiyar mahajjatan.

Mawallafi : Ahmed Salisu
Edita : Umaru Aliyu