1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jam'iyyar ADC ke kan gaba a zaben kasar Lesotho

Lateefa Mustapha Ja'afarMarch 2, 2015

Jam'iyyar Firaminstan kasar Lesotho Thomas Thabane ta ADC ce ke kan gaba a zaben 'yan majalisun dokokin kasar da aka gudanar.

https://p.dw.com/p/1Ejr7
Thomas Thabane
Hoto: Imago/Xinhua

Jam'iyyar ta ADC dai ta lashe zaben a yankuna 38 cikin 60 din da aka kammala kidaya kuri'un da aka kada. An dai gudanar da zaben ne a ranara Asabar din da ta gabata shekaru biyu gabanin lokacin da ya kamata a gudanar da shi domin dawo da doka da oda a kasar da ke yankin kudancin Afirka watanni shida bayan da aka zargi sojojin kasar da yunkurin juyin mulki. Jam'iyyar adawa ta DC karkashin jagorancin tsohon Firamminstan kasar Pakalitha Mosisili ce ke a matsayi na biyu bayan da ta lashe zaben a yankuna 20 na kasar yayin da jam'iyyar LCD karkashin jagorancin mataimakin Firaminstan na Lesotho ke mara mata baya a matsayin ta uku.