1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Shugaban kasar Sudan na kan hanyar komawa gida

Lateefa Mustapha Ja'afarJune 15, 2015

Jirgin Shugaba Omar al-Bashir na Sudan ya tashi daga Afirka ta Kudu a kan hanyarsa ta komawa gida duk kuwa da umurnin dakatar da shi da wata kotu a kasar ta bayar.

https://p.dw.com/p/1FhUd
Jirgin Al-Bashir ya bar Afirka ta Kudu zuwa Sudan
Jirgin Al-Bashir ya bar Afirka ta Kudu zuwa SudanHoto: picture-alliance/AP/A. Pretorius/Beeld/Netwerk24

Babbar kotun Afirka ta Kudu ce dai ta bayar da umurnin dakatar da al-Bashir bayan da ta ce ta samu takardar sammacinsa daga kotun kasa da kasa da ke hukunta masu aikata laifukan yaki, a yayin da yake halartar taron koli na kungiyar Tarayyar Afirka AU a birnin Johannesburg na Afirka ta Kudun. Ita dai kotun ta ICC na tuhumar Shugaba Bashir na Sudan da laifin kisan kiyashi da kuma aikata laifukan yaki a yayin rikicin yankin Darfur na Sudan din. Ana sa ran da zarar Bashir ya isa gida Sudan zai gudanar da taron manema labarai.