1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Al-Ka'ida ta kai hari a Burkina Faso

Abdul-raheem Hassan
February 28, 2017

Kungiyar 'yan ta'addan ta dauki alhakin harin da aka kai kan ofisoshin 'yan sanda biyu a birnin Ouagadougu na kasar Burkina Faso. Hukumomi sun ce maharan sun yi awon gaba da kadarori da dama.

https://p.dw.com/p/2YNf2
Islamisten Bewegung Jihad in West Afrika
Hoto: Getty Images

Kawo yanzu babu rahotannin asarar rai daga harin, sai dai an samu jikkatar wata jami'ar 'yan sanda. Wannan harin dai na zuwa ne a dai dai lokacin da birnin na Ouagadougou ke cike tsauraran matakan tsaro, ganin manyan baki na halartar bikin baje kolin fina-finan Afirka. Kungiyoyin da ke gwagwarmaya da makamai, na ci gaba da zama barazana ga kasar Burkina Faso, inda ake yawaita kai hare-hare da yin garkuwa da mutane. A watan Disemban da ta gabata kungiyar Ansarul Islam, ta yi ikirarin kai harin da ya hallaka dakarun soji 12 a kan iyakar kasar da Mali. A yanzu dai hukumomin kasar na ci gaba da zurfafa bincike dan gano mabuyar mayakan.