1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ambaliya ta hallaka mutane biyar a Sudan

August 3, 2020

Ruwan sama kamar da bakin kwarya ya hallaka tare da raba wasu mutane da dama da muhallansu a Sudan.

https://p.dw.com/p/3gLdB
Bangladesch I Flut in Bogra Sariakandi
Hoto: DW/M. Rashed

Mahukunta a kasar Sudan sun bayar da sanarwar mutuwar mutane 5 inda kuma wasu dubbai suka rasa mahallansu sanadiyar ambaliyar ruwa, inda ambaliyar ta yi awon gaba da gidaje kimanin gidaje sama da 3,500 

Tun a ranar Jumma'ar da ta gabata ce aka tafka ruwan da ya haddasa afkuwar lamarin, a cewar ministan cikin gida na Sudan  Eltrafi Elsdik a cikin wata sanarwar da ya fitar a ranar Litinin din nan.